banner
News center
Well-rounded experience in hospitality industry.

NDLEA ta kama ɗan fashin jeji da ake nema ruwa a jallo tare da kama jabun Dalar Amurka

Jan 01, 2024

Hukumar NDLEA ta kama wani dan fashi mai suna Aliyu Altine mai shekaru 19 da ake nema ruwa a jallo a kan titin Illela zuwa Sokoto a ranar Alhamis, 17 ga watan Agusta.

A cewar kakakin hukumar NDLEA, Mista Babafemi, an mika dan fashin jejin zuwa ga ‘yan sanda a jihar Sokoto domin ci gaba da bincike.

Hakazalika jami’an yaki da miyagun kwayoyi sun kama wasu jabun dalar miliyan 20 a yayin gudanar da aikin “Tsayarwa-da-Bincike” a kan babbar hanyar Lokoja zuwa Abuja.

Kakakin hukumar ta NDLEA ya bayyana a jiya Lahadi a Abuja cewa an gano kudaden ne na jabu a wata motar bas da ta taso daga Legas zuwa Abuja.

Ya bayyana cewa an kama direban motar mai shekaru 53, Onyebuchi Nlededin.

Log in to leave a comment